‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 15, Sun Jikkata Da Dama A Katsina

[ad_1]

Aƙalla mutane 15 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka jikkata a hare-haren daban-daban da ‘yan bindiga suka kai a ƙauyukan Dansoda da Jikamshi da ke ƙananan hukumomin Dandume da Musawa a Jihar Katsina.

A cewar ‘yansanda da mazauna yankunan, hare-haren sun faru ne a yammacin ranar Talata.

  • Babu Lokacin Da Aka Fi Bukatar Shawarar GGI Ta Shugaba Xi A Duniya Kamar Yanzu
  • Kamfanonin Ketare Na Ganin Sabbin Fa’Idodin Ci Gaba Daga Sabbin Bukatun Kasuwar Sin

Wani mazaunin Dansoda, Kabir Adamu, wanda ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a ranar Laraba, ya ce ‘yan bindigar sun kutsa cikin ƙauyen ne da misalin ƙarfe 8:00 na dare, inda suka kashe mutane 11 nan take.

A wani hari na daban kuma, an ruwaito cewa mutane huɗu sun mutu lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari a garin Jikamshi da ke ƙaramar hukumar Musawa.

Dukka wadanda suka rasa rayukansu, an riga an binne su bisa ga koyarwar addinin Musulunci.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *