Togo Na Neman Ƙarin Wutar Lantarki Da Take Siya Daga Nijeriya

[ad_1]

Togo ta bayyana sha’awarta na ƙara yawan wutar lantarki da take saya daga Nigeria ta hannun ‘Niger Delta Power Holding Company’ (NDPHC), domin samar da wutar ga sabbin wuraren da ake buƙatar wutar lantarkin a kasar.

An bayyana wannan buƙatar ne yayin wani muhimmin taro tsakanin shugabannin NDPHC da wata tawaga daga kamfanin samar da wutar lantarki na kasar Togo mai suna ‘Compagnie Énergie Électrique du Togo (CEET)’.

  • Nijar Ta Haramta Fitar Da Dabbobi Ketare Don Takaita Karancinsu A Cikin Gida
  • Wane Irin Tanadi Kuka Yi Wa Sallah Karama A Wannan Lokacin?

Tawagar ta samu jagoranci daga babban daraktan kamfanin, Débo-K’mba Barandao, wanda ya kai ziyara ga shugabannin NDPHC domin ƙarfafa haɗin gwiwar dake tsakaninsu tare da duba yiwuwar faɗaɗa kasuwancin wutar lantarki tsakanin ƙasashen.

Kamfanin CEET, wanda hedikwatarsa ke Lomé, a halin yanzu yana sayen kusan megawatt-hours 75 (MWh) na wutar lantarki daga NDPHC. Wannan tsarin samar da wutar ya taimaka wa Togo wajen tabbatar da daidaiton samar da lantarki da kuma tallafawa harkokin tattalin arziƙin ƙasar.

Wutar lantarkin da ake shigowa da ita daga Nijeriya tana taimakawa wajen samar da ingantacciyar wuta mai araha ga gidaje, kasuwanni da kuma cibiyoyin gwamnati a Togo.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *