Tashar Arewa24 ta dawo da shirin Zaɓi Biyu a zango na biyu

[ad_1]



Tashar AREWA24 ta sanar da dawo da shahararren shirin nan na wasan kwaikwayo mai dogon zango, “Zaɓi Biyu” bayan azumin watan azumi na Ramadan.

Tashar ta bayyana cewa sabon zangon na zuwa ne bayan gagarumar nasarar da zangon farko ya samu, inda ya ja hankalin masu kallo a Arewacin Najeriya da ma sauran wurare.

Shugaban Arewa24, Celestine Umeibe, ya ce shirin ya samu karɓuwa sosai saboda yadda ya nuna rayuwar soyayya, zaɓi, da ƙalubalen zamantakewa a cikin al’adar Hausawa.

Ya ƙara da cewa zango na biyu zai zo da sabbin abubuwa masu ƙayatarwa, ciki har da zurfin labari, bunƙasar halayen jarumai, da kuma sabbin sauye-sauye masu ba da mamaki.

“A cikin wannan sabon zangon, masu kallo za su ga yadda jaruman ke fuskantar sakamakon zaɓin da suka yi a baya, da kuma sabbin ƙalubale masu tasiri dangantaka da burinsu,” in ji Umeibe.

Shi ma daraktan shirin, Salisu Balarabe, ya ce “Zaɓi Biyu” na ɗauke da labari da ke haska rayuwar yau da kullum ta al’umma, tare da ƙarin zurfi da sosa zuciya a zango na biyu.

Ya ce an ƙara inganta shirin ta yadda zai ci gaba da nuna al’adu, harshe da kuma abubuwan da suka shafi rayuwar Hausawa, musamman matasa.

Kamfanin ya kuma bayyana cewa shirin na bai wa masu talla damar isa ga masu kallo masu yawa a cikin Hausawa, musamman matasa da ke bibiyar shirye-shiryen talabijin.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *