Shugabar Ma’aikatan Abuja ta rasu
[ad_1]
Allah Ya yi wa Shugabar Ma’aikata ta Babban Birnin Tarayya, Abuja, Misis Grace Adayilo, rasuwa a safiyar Litinin ɗin nan.
Shaidu sun tabbatar wa wakilinmu cewa ta rasu ne ’yan sa’o’i kaɗan da suka gabata. Kodayake kawo yanzu ba a sanar da rasuwar a hukumance ba.
Misis Grace Adayilo ita ce mace ta farko kuma ’yar asalin yankin Babban Birnin Tarayya ta farko da ta riƙe wannan muƙami.
ta kasance tsohuwar Sakatariyar Ilimi ta Ƙaramar Hukumar Birnin Abuja (AMAC), kafin Minista Nyesom Wike, ya naɗa ta Shugabar Ma’aikata.
Ita ce ta wakilci Wike a babban taron Majalisar Taro ta Ƙungiyar G-7 da aka gudanar a ranar Larabar da ta gabata a Abuja.
Ko a ranar Lahadi ta samu halartar ibada a coci, inda washegari aka samu labarin safiyar Litini.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link