Shirin Sauya Sheƙa: An Tsaurara Tsaro A Harabar Gidan Gwamnatin Kano

[ad_1]

Rundunonin jami’an tsaro sun hallara ciki da wajen harabar gidan Gwamnatin Kano a ranar Litinin, yayin da ake samun rahotannin shirin ficewar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa Jam’iyyar APC.
Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa, rundunonin jami’an tsaron sun hada da na ‘Yansandan Nijeriya, da na tsaro cikin gida (DSS), a babbar ƙofar shiga gidan Gwamnatin.
  • Xi Jinping Ya Amsa Wasikar Malamai Da Dalibai Na Tawagar Mu’amalar Matasa Ta Amurka
  • Sin Da Tanzania Sun Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwa
Duk da cewa, ba a tabbatar da shirin ficewar a hukumance ba, amma ana kyautata zaton gwamnan yana shirin komawa Jam’iyyar APC.
An ga a kalla motoci masu silke na ‘yansanda da na DSS guda bakwai, inda aka jibge su a wurare daban-daban masu mahimmanci, ciki har da babbar ƙofar shiga, da kuma hanyar da ke kaiwa ga gidan Gwamnatin.
Har ila yau kuma, an kuma ƙarfafa binciken tsaro, ga duk wanda zai shiga gidan Gwamnatin.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *