Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027

[ad_1]


Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayyana cewa jam’iyyar APC mai mulki za ta samu kashi 95 na kuri’un da aka kada a zaben 2027.

Gwamna Sani ya yi karin haske da cewa, jam’iyyar APC tana da ‘yan majalisar wakilai hudu ne kawai a shekarar 2023, inda ya bayyana cewa jam’iyyar a yanzu tana da mambobi goma sha uku (13) a zauren majalisar.

Da yake jawabi ga wasu jiga-jigan jam’iyyar APC a babban taron gangamin da aka gudanar a Kaduna a karshen mako, Gwamna Sani ya ce, biyo bayan sauya sheka zuwa APC, a yanzu APC na da ‘yan majalisar wakilai 13 daga jihar Kaduna, inda jam’iyyar adawa ta PDP ke da uku kacal.

Ya kara da cewa, a majalisar dokoki ta jihar, APC ce ke da rinjaye da mambobi 26 inda PDP ke da mambobi takwas kacal.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *