Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki a Janairu 1, 2026 — Tinubu
[ad_1]
Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa aiwatar da sabbin dokokin harajin Nijeriya zai fara aiki a ranar 1 ga Janairu, 2026, kamar yadda aka tsara.
A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu da kansa a ranar Talata, Shugaban ya ce sabbin dokokin haraji, gami da wadanda suka fara aiki a ranar 26 ga Yuni, 2025, da kuma sauran wadanda aka tsara za su fara a ranar 1 ga Janairu, 2026, kamar yadda aka tsara.
- Gwamnatin Ghana Ta Sake Buɗe Matatar Man Fetur Bayan Rufe Ta A Baya
- An Yi Taron Ayyukan Noma Na Kwamitin Tsakiyar Kasar Sin A Beijing
Tinubu ya bayyana gyare-gyaren tsarin harajin a matsayin wata dama ta sau daya a ƙarni don gina tattalin arzikin kasa mai juriya da nagarta.
A cewar Tinubu, dokokin haraji ba an tsara su ne don kara yawan haraji ba, sai don tallafawa dokokin game da tsayawa da kafarsu, samar da daidaito da kare mutunci, sannan za su karfafa tsarin zamantakewa.
Tinubu ya amince da cewa, gwamnatinsa ta san damuwar jama’a game da batun sauye-sauyen da ake zargin an yi wa wasu dokokin harajin da Majalisa ta zartar a kwanan nan, amma ya jaddada cewa babu wata babbar matsala game da sauye-sauyen da za ta sanya a dakatar da aiwatar da tsare-tsaren.
[ad_2]
Source link