Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara
[ad_1]
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya kare salon mulkinsa na tsawon shekaru takwas da ya yi a jihar, inda ya jaddada cewa ya tabbatar da adalci da daidaito tsakanin kowane ɓangare, tare da ƙin amincewa da abin da ya kira “haƙƙoƙin mu ne” daga mutanen Kudancin Kaduna.
Da yake jawabi a shirin ‘Social siyasa‘ na tashar talabijin ta Channels, El-Rufai ya ƙaryata zargin nuna son addini, yana mai cewa manufofinsa sun shafi kowa, ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.
Ya bayyana cewa wasu mutane daga Kudancin Kaduna sun saba samun fifiko a ƙarƙashin gwamnatocin da suka gabata, wanda shi ya dakatar da shi da gangan, kana ya zargi wasu shugabannin Kirista daga yankin suna cin moriyar wasu tallafin kuɗi da gwamnatinsa ta daina bayarwa.
Game da batun wakilci a gwamnati, El-Rufai ya musanta iƙirarin wariya, yana mai cewa naɗe-naden muƙaman gwamnati an riƙa yin su bisa daidaito tsakanin kowace mazabar sanata, ba wai bisa addini ko ƙabilanci ba.
Kan batun goyon bayansa ga tikitin musulmi-musulmi na jam’iyyar APC a zaɓen 2023, El-Rufai ya ce tsantsar dabarar siyasa ce kawai, kuma duk wani ɗan siyasa yana tafiya da lissafin yadda zai kai ga samun nasarar ne.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp
[ad_2]
Source link