Nnamdi Kanu: Masu zanga-zanga sun yi watsi da gargaɗin ’yan sanda

[ad_1]



’Yan sanda da jami’an tsaron farin kaya (DSS) sun shiga shirin ko-ta-kwana a birnin Abuja bayan masu zanga-zangar neman a saki shugaban ’yan awaren Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu, sun yi watsi haramcin kotu kan yin hakan a kusa da Fadar Shugaban Ƙasa.

An shirya zanga-zangar ce ƙarƙashin jagorancin tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa kuma mai fafutukar #RevolutionNow, Omoyele Sowore, domin matsa wa gwamnati lamba ta saki Kanu, wanda ke tsare tun shekarar 2021, kan zargin ta’addanci da cin amanar ƙasa.

Shaidu sun bayyana cewa an fara sanya shingayen bincike a wasu manyan hanyoyi da ke kaiwa Majalisar Dokoki ta Ƙasa, hedkwatar rundunar ’yan sanda, dandalin Eagle Square da Kotun Ɗaukaka Ƙara tun ranar Lahadi.

Nnamdi Kanu, wanda ke fuskantar tuhumar ta’addanci da cin amanar ƙasa, an fara kama shi a 2015, aka ba shi beli a 2017, kafin ya tsere bayan harin da sojoji suka kai gidansa a Abia.

Duk da cewa kotuna da dama sun bayar da umarnin a sake shi, Gwamnatin Tarayya ta ƙi bin hukuncin, abin da ke haifar da ƙarin fushi da nuna rashin jin daɗi daga jama’a.

Da yake jawabi kafin zanga-zangar, Sowore ya ce za su ci gaba da tafiyar da shirin kamar yadda aka tsara, yana mai jaddada cewa ’yan Najeriya na da cikakken ’yancin yin zanga-zanga cikin lumana.

“Tsare Nnamdi Kanu ba bisa doka ba ne, kuma abin kunya ne ga ƙasa,” in ji Sowore. “Kotun Ɗaukaka Ƙara ta wanke shi tun 2022, amma gwamnati ta ƙi bin hukuncin.”

Ya kuma roƙi sabon Kwamishinan ’Yan Sanda na Abuja da kada ya yi amfani da ƙarfi wajen tarwatsa masu zanga-zangar.

“Duk wani jami’i da ya ci zarafin masu zanga-zanga za a ɗauki mataki a kansa. Lokaci ya wuce da ake danniya da take haƙƙin jama’a,” in ji Sowore.

Sai dai Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, ya umurci jami’ansa su tabbatar da bin umarnin kotun tarayya da ta hana gudanar da zanga-zanga a kusa da Fadar Shugaban Ƙasa da wasu wurare masu muhimmanci a Abuja.

“Rundunar ’yan sanda za ta ci gaba da tabbatar da doka da oda bisa tsarin mulki,” in ji mai magana da yawun rundunar, Benjamin Hundeyin.

“Duk wanda ya karya doka ko ya tayar da hankalin jama’a za a kama shi kuma a gurfanar da shi.”

A cewar ’yan sanda, matakin na nufin kare tsaron ƙasa da hana tashin hankali a muhimman wuraren gwamnati.

A nasa bangaren, masanin harkokin tsaro kuma shugaban cibiyar RULAAC, Mista Okechukwu Nwanguma, ya gargaɗi gwamnati da ta guji amfani da ƙarfi wajen murƙushe masu fafutuka, yana cewa hakan na iya tayar da ƙarin fitina.

“Kungiyar IPOB ta samo asali ne daga jin an ware su da rashin adalci,” in ji shi. “Idan gwamnati ta saki Kanu ta hanyar tattaunawa da bin doka, hakan zai taimaka wajen kawo zaman lafiya a kudu maso gabas.”

Ya kuma bukaci gwamnati ta rage amfani da ƙarfin sojoji a yankin, ta ƙarfafa ’yan sanda na al’umma, tare da magance matsalolin rashin aiki, talauci da jin wariya.

A cewarsa, lamarin Nnamdi Kanu gwaji ne ga gwamnatin Najeriya wajen tabbatar da adalci, hadin kai da mutunta dokar ƙasa.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *