NECO ta sake jaddada nasarar ɗaliban Kano a jarrabawar bana
[ad_1]
Hukumar Shirya Jarrabawar Kammala Sakandare a Nijeriya (NECO) ta jaddada cewa Jihar Kano ce ta fi kowace jiha samun nasara a sakamakon jarrabawar bana, tana mai ƙaryata rahoton da jaridar Premium Times ta fitar, wanda ya ce Jihar Abia ce ke kan gaba.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa rahoton da jaridar Premium Times ta wallafa ba shi da tushe balle makama, inda ta bayyana shi a matsayin mai cike da ruɗu da rashin inganci.
“Rahoton ya ce bayan bincike da kuma nazarin bayanan sakamakon jarrabawar bana, Premium Times ta tabbatar cewa ba Kano bace jiha mafi nasara, kamar yadda NECO ta bayyana a baya,” in ji rahoton.
Kazalika, binciken na Premium Times ya ƙara da cewa kwata-kwata Jihar Kano ma ba ta shiga cikin jihohi 10 da suka yi nasara ba, bal ma ta zo ne a matsayi na 29 daga cikin 37.
Sai dai NECO ta musanta wannan iƙirari, tana mai cewa alƙaluman da ta fitar sahihai ne, kuma an samo su ne bisa ingantaccen tsarin ƙididdiga da hukumar ke bi a duk shekara.
Ana iya tuna cewa, cikin sakamakon jarrabawar wannan shekara ta 2025 da Hukumar NECO ta fitar, ya nuna cewa kashi 60.26 cikin 100 ne suka samu kiredit biyar zuwa sama ciki har da darussan Lissafi da Turanci.
Shugaban hukumar Farfesa Ibrahim Wishishi ya shaida wa BBC cewa Jihar Kano ce kan gaba a yawan ɗaliban da suka samu nasara a jarrabawar a faɗin wuraren da hukumar ke shirya jarrabawar da suka haɗa da wasu ƙasashen Afirka.
Da take mayar da martani cikin wata sanarwa da gwamnatin Kanon ta fitar, ta ce wannan ne karon farko cikin shekara 25 da jihar ta samu wannan nasara.
Shugaban na NECO ya ce cikin ɗalibai 1,358,339 da suka rubuta jarrabawar, yayin da 818,492 ne suka samu kiredit a darussa biyar da suka haɗa da Turanci da Lissafi.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link