Najeriya za ta fafata da Masar domin neman na uku a gasar AFCON

[ad_1]



Tawagar ƙwallon ƙafa ta Nigeria, Super Eagles, za ta kece raini da ƙasar Masar a wasan neman mataki na uku na gasar Kofin Nahiyyar Afirka da ke gudana a Morocco.

Kasashen za su yi karon-battar ne a da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Asabar, gabanin buga wasan ƙarshe na gasar da za a yi da ƙarfe 8 na dare a ranar Lahadi tsakanin Senegal da Morocco.

Duk a jiya Laraba ce a ƙasashen biyu suka rashin nasara a wasan kusa da na ƙarshe da suka fafata, inda Senegal ta yi ta yi waje rod da Masar, yayin da Morocco ta yi galaba a kan Najeriya bayan wasan da suka fafata ya kai su zuwa bugun fanareti.

Cikin wasanni 7 na baya da ƙasashen suka fuskanci juna, Masar ta yi nasara sau 4, yayin da Najeriya ta yi nasara sau 2, sannna kuma aka yi canjaras sau 1.

A cikin dukkanin wasannin da suka fuskanci juna a baya, Masar ta samu nasarar zura ƙwallaye 10 yayin da Najeriya ta zura ƙwallaye 7 a raga.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *