Mutum 3 sun shiga hannu kan sace tagogin makaranta a Gombe

[ad_1]



Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da fasa makarantar firamare ta Magaba da ke Bajoga, a Ƙaramar Hukumar Funakaye, a Jihar Gombe.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama su ne bayan shugaban makarantar, Malam Buba Chiroma, ya kai rahoto ofishin ’yan sanda a ranar Juma’a, 22 ga watan Agusta, 2025.

Chiroma, ya bayyana cewa da misalin ƙarfe 8:20 na safe ne aka gano an fasa tagogin makarantar, amma ba su san waɗanda suka aikata laifin ba.

DSP Abdullahi, ya ce bayan kai rahoton, jami’an tsaro tare da ’yan sa-kai suka je wajen, inda suka cafke mutum uku da ake zargi kuma suka ƙwato wasu tagogi da aka lalata a matsayin shaida.

Ya ƙara da cewa bincike yana gudana, kuma za a sanar da al’umma abin da ake ciki.

Haka kuma, ya yi kira ga jama’a da su taimaka wajen tsaron makarantu musamman a lokacin ake hutu, tare da sanar da ’yan sanda duk wani abu da suke da shakku a kai.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *