Ministan Yaɗa Labarai Ya Gargaɗi Matasa Kan Yaɗa Labaran Ƙanzon Kurege

[ad_1]

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai na Ƙasa, Mohammed Idris, ya yi gargaɗin cewa yaɗa bayanan ƙarya na haifar da manyan ƙalubale na ɗabi’a da na ƙasa, tare da kira ga matasan Nijeriya da sauran ’yan ƙasa da su riƙa tantance gaskiyar duk wani bayani kafin su yaɗa shi.

Da yake jawabi a taron laccar Azumin Ramadan ta haɗin gwiwa karo na 20 da gidan talabijin na NTA, da Gidan Rediyon Faransa (FRCN) da Mutyar Nijeriya (ƁON) suka shirya a Kaduna jiya, ministan ya yi kashedin cewa rashin amfani da dandalin zamani yadda ya kamata na iya ƙara rarrabuwar kai tare da raunana haɗin kan ƙasa idan ba a tafiyar da su bisa alhaki da gaskiya ba.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci Matasa Su Riƙa Tantance Sahihancin Labari Kafin Su Yaɗa Shi
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Ministan ya jaddada cewa duk da cewa fasahar zamani ta dijital na kawo manyan damammaki, tana kuma tafe da jarabawar ɗabi’a da ke buƙatar ladabi da ɗaukar alhaki. Ya ƙara da cewa tabbatar da sahihancin bayanai ya zama wajibi na ɗan ƙasa da kuma na ɗabi’a.

Haka kuma, ministan ya bayyana shirye-shiryen ƙarfafa matasa da dama a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, waɗanda ke amfani da fasaha a matsayin hanya ta samar da damar tattalin arziki.

Ya lissafo tsare-tsare irin su shirin 3 Million Technical Talent (3MTT), da Asusun Lamunin Ilimi na Nijeriya (NELFUND), da kuma kafa cibiyar farko a Afirka ta Ilimin Kafofin Yaɗa Labarai da Ilimin Tantance Bayanai (Media and Information Literacy Institute).

A cewarsa, ilimin kafofin yaɗa labarai shi ne “rigakafin” yaɗa bayanan ƙarya, kuma waɗannan ƙoƙari an tsara su ne domin bai wa matasan Nijeriya ƙwarewar da za su buƙata domin samun nasara a tattalin arzikin dijital.

Ministan ya lura cewa yawan matasan da Nijeriya ke da su na ɗaya daga cikin manyan ƙarfinta, amma ya yi gargaɗin cewa makomar ƙasar na rataye ne kan yadda ake shiryawa da tallafa wa matasa yadda ya kamata.

“Ƙasar da ta gaza kula da matasanta ba ta da makoma. Muna zuba jari a tsari mai ɗorewa inda fasahar dijital za ta zama matakala ta samun dama,” in ji shi.

Ya kuma buƙaci matasan Nijeriya da su yi amfani da dandamalin dijital wajen ayyuka masu amfani kamar ilimi, ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban ƙasa.

“Ku tantance kafin ku yaɗa. Ku dakata. Ku binciki tushen labarin,” in ji shi, yana mai ƙarawa da cewa dole ne a yi amfani da kayan aikin dijital wajen ƙarfafa haɗin kai, ilimi da ci gaba maimakon haifar da rarrabuwar kai.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *