Manoma sun yi asarar miliyoyin Naira a Taraba
[ad_1]
Sanadiyyar ambaliyar ruwa a gonaki amfanin gona na miliyoyin Naira ne suka salwanta inda ɗaruruwan filayen noma suka shefe da ruwa a Jihar Taraba.
Kodayake, ba a bayyana ko an sako ruwa daga Logdo Dam ba ne daga jamhuriyar Kamaru ba, amma kogin Benuwe da ke Taraba ya yi ta malala daga gaɓarsa wanda ya yi sanadin ambaliya da lalata ɗaruruwan filayen noma.
Daily Trust ta gano cewa ruwan ya fara ƙaruwa a kogi a ’yan kwanakin da suka gabata, kuma a yanzu kogin ya yi ta malala a gefan koguna inda ya haddasa ambaliya a faɗin jihar.
Ambaliyar ta shafi wasu yankunan sassan Ƙananan hukumomin Lau da Karim_Lamido da Gassol da Ardo-kola
Gonakin da ambaliyar ta shafa sun haɗa da: Da na Shinkafa da Masara galibi da ke kusa da kogin Benuwe sun lalace yayin da gidaje da dama a ƙauyukan da ke gefen kogin Benuwe kuma suka nutse.
Alhaji Sale Binnari, a Ƙaramar hukumar Karim-Lamido ya shaida wa Daily Trust cewa ruwa ya lalata ɗaruruwan gonakin shinkafa da masara.
Garba Halilu, a garin Mutum-Biyu, Ƙaramar hukumar Gassol ya kuma shaida wa Daily Trust cewa, ambaliyar ruwa ta lalata gonaki da dama a yankunan Mutum Biyu da yankin Kwatan Nanido da Maigemu da Sheka.
Ya ce, kogin ya malala a rassan gaɓarsa, sakamakon haka ɗaruruwan filayen noma ne suka nutse da ruwa.
Hakimin kauyen Sheka a Ƙaramar hukumar Gassol, Alhaji Haruna Sheka ya kuma ce gonaki da dama sun nutse da ruwa sakamakon ambaliya da ruwan kogin Benuwe.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link