Majalisar Dattawa za ta yi zaman gaggawa a ranar Talata

[ad_1]



Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya umarci dukkanin Sanatoci su koma Majalisa domin zaman gaggawa a ranar Talata, 10 ga watan Fabrairu, 2026.

An kira wannan zama ne kwanaki kaɗan bayan Majalisar Dattawa ta ƙi amincewa da ƙudirin da ke neman a riƙa tura sakamakon zaɓe ta lantarki.

A wata sanarwa da Magatakardar Majalisar, Emmanuel Odo, ya fitar, an buƙaci dukkanin sanatoci su halarci zaman.

Za a fara zaman gaggawar da misalin ƙarfe 12 na ranar Talata.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *