Kotu Ta Janye Tuhume-tuhumen Da Ake Yi Wa Sanata Natasha
[ad_1]
Wata Babbar Kotu da ke Abuja ta janye dukkanin tuhume-tuhumen da gwamnatin tarayya ta shigar a kan Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya.
Gwamnatin ta janye ƙarar ne bayan ofishin Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya ya shigar da takardar dakatar da ƙarar.
- Zargin Almundahanar ₦1.35bn: Kotun Ƙoli Za Ta Warware Taƙaddamar EFCC Da Lamiɗo
- Gwamnatin Kaduna Ta Ce Shari’ar Zidan Ta Gudana Cikin Gaskiya da Adalci
An danganta shari’ar da wasu kalamai da ake zargin Sanatan ta yi a wata hira a gidan talabijin.
Alƙalin kotun Mai shari’a, Justice C. N. Oji, ya amince da janye ƙarar, inda ya ce hakan na nuna buƙatar yin taka-tsantsan wajen amfani da ikon gurfanarwa.
Bayan hukuncin, Sanata Akpoti-Uduaghan ta ce wannan mataki ya wanke ta, tare da jaddada ƙudirinta na ci gaba da yi wa al’ummarta hidima da kare dimokuraɗiyya.
[ad_2]
Source link