Jami’an tsaro sun tsare jagoran Falasdinawa mazauna Najeriya
[ad_1]
Jami’an tsaron Najeriya sun yi awon gaba da Shugaban al’ummar Falasdinawa mazauna Najeriya, Abu Ramzi Ibrahim, a birnin Abuja
Rahotanni sun suna jami’an tsaro sun kama Abu Ramzi Ibrahim me a gidansa da ke Abuja tun ranar Juma’a.
Majiyoyi daga cikin al’ummar Falasɗinu sun ce Ibrahim, wanda dasn Bafalasɗine ne kuma ya yi karatu a jami’ar Najeriya, yana tsare har zuwa yanzu.
Wakilinmu ya yi ƙoƙarin jin ta bakin Jakadan Falasɗinu da ke Najeriya amma hakarsa ta cin ma ruwa ba.
Ibrahim ya shahara wajen kare muradun Falasɗinawa ta kafafen yaɗa labarai, musamman a ’yan watannin nan da rikicin Isra’ila da Falasɗinu ke ƙara ɗaukar hankalin duniya.
Har zuwa yanzu babu wata sanarwa daga hukumomin tsaro kan batun kama shi.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link