Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

[ad_1]

Fadar Shugaban Ƙasa, ta ce ba gaskiya ba ne cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba shi da lafiya kuma ana shirin kai shi ƙasar waje domin nema masa magani.

A makon da ya gabata, cibiyar binciken labarai ta ICIR ta ce ta samu labari daga wata majiyarta cewa tawagar likitocin shugaban ƙasa na shirin fitar da shi waje domin jinya.

ICIR ta rubuta a shafinta cewa rahotanni na nuna shugaba Tinubu yana kwance ba ya iya fita.

Hakan ya sa ba ya gudanar da wasu ayyukan mulki.

A cewar rahoton, Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya wakilce shi a wasu ayyukan gwamnati.

Sai dai wasu daga cikin hadiman shugaban kamar Abdulaziz Abdulaziz, mai taimaka masa a kafafen watsa labaru, ya ce labarin ba gaskiya ba ne.

Batun rashin lafiyar Tinubu ba sabon abu ne, domin tun yana yaƙin neman zaɓen takara a 2023 ake kai ruwa rana kan batun.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *