Dangote Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Da Tsohon Shugaban NMDPRA A ICPC

[ad_1]

Lauyan Aliko Dangote, Dakta O.J. Onoja, SAN, ya rubuta wa Hukumar Kula da Ayyukan Cin Hanci da Rashawa Mai Zaman Kanta (ICPC) wasiƙa, inda ya nemi a janye karar da mai gidansa ya shigar da Injiniya Farouk Ahmed, tsohon shugaban hukumar NMDPRA.
Wasikar da aka rubuta wa ICPC mai kwanan wata 5 ga Janairu, 2025, mai taken “Sanarwar Janye Karar Da Aka Shigar Kan Injiniya Farouk Ahmed,” ta bayyana cewa, wata hukumar gwamnati da ba a ambaci sunanta ba ta karɓi ragamar binciken.
Da yake mayar da martani kan wannan wasika, kakakin ICPC, John Odey, ya bayyana cewa, duk da bukatar janye karar amma za a ci gaba da bincike domin ICPC na aiki ne don kare martabar kasa daga masu zagon kasa ga tattalin arzikin kasa.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *