Chelsea ta kammala ɗaukar Garnacho daga Manchester United

[ad_1]



Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea ta tabbatar da ɗaukar ɗan wasan gaban Manchester United, Alejandro Garnacho, kan kuɗin da ya kai kusan fam miliyan 85 (£85m).

Rahotanni sun bayyana cewa ɗan wasan na ƙasar Argentina ya rattaba hannu kan kwantiragin zama a Stamford Bridge har zuwa shekarar 2032.

Garnacho, mai shekara 21, zai riƙa ɗaukar albashin fam 250,000 duk mako, kwatankwacin Naira miliyan 500 a kuɗin Nijeriya, lamarin ya sanya shi a sahun manyan ’yan wasa mafiya albashi a Stamford Bridge.

A bara ne tauraruwarsa ta haska a Manchester United, bayan ya ci ƙwallo 11 ya kuma ba da gudunmawar zura wasu 10 a raga.

A jimilla, ya buga wasanni 144 tun daga lokacin da aka ɗaukoshi daga Atlético Madrid a 2020, inda ya ci ƙwallo 26.

Ana iya tuna cewa Garnacho yana cikin ’yan wasa biyar da suka nemi barin United, ciki har da Marcus Rashford, Antony, Tyrell Malacia da Jadon Sancho, bayan wata matsala da ta shafi sabon tsarin koci a Old Trafford.

Kociyan Chelsea, Enzo Maresca, ya bayyana farin ciki da wannan cafane da aka yi, inda ya ce Garnacho zai ƙara wa ƙungiyar kuzari da saurin kai hare-haren a wasanninta.

“Ɗan wasa ne da yake iya sauya salon wasanni da kansa, kuma hakan zai taimaka wajen dawo da Chelsea cikin sahun manyan ƙungiyoyin masu neman kofuna,” in ji shi.

Masu sharhi sun ce wannan matakin zai ƙara armashi da zafi a gasar Premier League, musamman ganin yadda Garnacho ya saba taka rawar nuna kansa a manyan wasanni.

Sai dai da dama daga cikin magoya bayan Manchester United sun nuna takaicinsu kan cefanar da ɗan wasan da aka yi, inda suke ganin bai kamata a sayar da shi ba saboda a gina ƙungiyar da shi tare da sauran matasan ’yan wasan da ke nuna hazaƙa.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *