Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

[ad_1]


A yau Litinin aka bude wani taro na masu mukamin magajin gari ko wakilansu da jami’an diplomasiyya da malamai daga kasashe 10, a birnin Dunhuang dake kan hanyar Siliki a lardin Gansu na arewa maso yammacin kasar Sin.

Makasudin taron shi ne, tattauna damarmaki da kalubalen da tafiyar da ayyukan kare al’adu ke fuskanta a birane.

Yayin da ake fama da karuwar kaura zuwa birane a duniya, mahalartar taron sun jadadda muhimmancin daidaita ayyukan kare al’adu da na raya birane. Sun nanata bukatar karfafa hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa a matsayin wata hanya ta tunkarar wadannan kalubale na bai daya.

A matsayin birnin dake karbar bakuncin taron, Dunhuang mazauni ne ga wurare 3 dake cikin jerin wuraren gargajiya na hukumar UNESCO da kuma wuraren kayayyakin gargajiya sama da 260, wanda kuma ke nuna hadaddun dabarun da aka dauka a shekarun baya-bayan nan da nufin kare al’adun gargajiya yayin da ake bunkasa birnin. (Fa’iza Mustapha)

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *