AFCON 2025: Nijeriya Ta Kai Zagayen ‘Yan 16 Bayan Doke Tunisia

[ad_1]

Tawagar ƙwallon ƙafa ta Nijeriya da ke buga gasar kofin ƙasashen nahiyar Afirika yanzu haka a ƙasar Morocco ta samu nasarar kai wa matakin zagayen ‘yan 16 bayan ta doke ƙasar Tunisia a wasa na biyu da ta buga a rukunin C na gasar.

Nijeriya ta zama ƙasa ta biyu bayan Masar da ta samu nasarar tsallakawa zuwa matakin zagayen 16 a gasar.

  • Majalisar Dokokin Kasar Sin Ta Kammala Zaman Zaunannen Kwamitinta
  • AFCON 2026: DR Congo To Yi Wa Senegal Fankale

Super Eagles ta haɗa maki 6 da ƙwallaye biyu a wasanni biyu da ta buga, yayin da aka jefa mata ƙwallaye uku a wasa biyu.

Victor Osimhen ne ya fara jefa ƙwallo a ragar Tunisia tun kafin zuwa hutun rabin lokaci, bayan an dawo ne kyaftin ɗin Nijeriya Wilfried Ndidi ya jefa ƙwallon ta biyu a minti na 51 kafin Ademola Lookman ya jefa a minti na 67.

Wasan na yau ya kasance mai matuƙar armashi duba da cewa dukkanin ƙasashen biyu ba kanwar lasa ba ne a fagen taka leda a Afirika.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *