Nenadi Usman Ta Fara Aiki A Ofishin jam’iyyar LP Amatsayin Shugaba
[ad_1]
Sanata Nenadi Usman ta fara aiki a ofishin jam’iyyar Labour Party (LP) na kasa da ke Abuja. Kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar Labour Party, wanda Sanata Nenadi Usman ke jagoranta, ya fara aiki a ofishin jam’iyyar na kasa a Abuja a ranar Talata, bayan hukuncin kotu da ya tabbatar da jagorancinta.
Usman tare da mambobin tawagarta sun isa ofishin jam’iyyar da misalin karfe 11 na safe.
- Wani Mutum Ya Rasu Yayin Ciro Tukunyar Gas Daga Cikin Rijiya A Kano
- Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke Biyo Bayan Sace Iyalai A Kaduna
An cire manyan hotuna da tallace-tallacen tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Julius Abure, da suka mamaye harabar ofishin a baya, sannan aka maye gurbinsu da manyan hotunan Sanata Usman, wanda ya nuna sauyin jagoranci a fili bayan hukuncin kotu da ya tabbatar da ita a matsayin shugaba.
Masu goyon bayan jam’iyyar da mambobi da dama sun taru a kusa da ofishin suna jiran ci gaba da faruwa yayin da harkokin jam’iyyar suka fara motsi a hankali. Yanayin ya kasance cikin natsuwa tare da nuna alamar jiran abin da da dama suka bayyana a matsayin muhimmin lokaci ga jam’iyyar.
Fara aikin Sanata Usman ya zo ne kwanaki bayan hukuncin kotu da ya kawo karshen rikicin shugabanci da ya daɗe a jam’iyyar, wanda ya ba ta damar karɓar cikakken ragamar jagorancin jam’iyyar.
[ad_2]
Source link