Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC
[ad_1]
Majiyoyi a jam’iyyar APC sun bayyana cewa tattaunawar da aka yi da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ta rushe ne bayan ya gabatar da buƙatu masu yawa da suka haɗa da neman iko a manyan tsare-tsaren jam’iyyar da kuma neman kujerar mataimakin shugaban ƙasa.
Sabbin bayanai sun bayyana a ranar Alhamis cewa ƙoƙarin fadar shugaban ƙasa da APC na ƙulla yarjejeniya da tsohon gwamnan Kano wanda a baya ake kallonsa a matsayin “amaryar siyasa” mai tasiri ya ƙare ba tare da cimma matsaya ba.
- Gwamna Yusuf Zai Yi Nadamar Barinmu – Kwankwaso
- Tinubu Da Kwankwaso Za Su Gana Yayin Da Siyasar Kano Ta Ɗauki Sabon Salo
An ce Kwankwaso, jagoran Kwankwasiyya da NNPP, an nemi haɗin gwiwarsa ne saboda tasirin siyasar jar hularsa da rawar da jam’iyyarsa ta taka a zaɓen 2023. Majiyoyi da ke da masaniya kan tattaunawar sun shaida wa jaridar YAU cewa ganawar tsakanin Kwankwaso da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta gudana na tsawon awanni, musamman a Abuja, domin samar da tsani zuwa Kano da sassan Arewa maso Yamma.
Sai dai manyan majiyoyi a APC sun ce tattaunawar ta samu tsaiko ne kan abin da suka kira buƙatun da suka wuce gona da iri. A cewarsu, Kwankwaso ya nemi a ba shi ikon kusan kashi 20 cikin 100 na tsare-tsaren jam’iyyar a matakin ƙasa, tare da neman kujerar mataimakin shugaban ƙasa da kuma tabbaci har zuwa zagayen siyasar 2031—abin da ya tayar da ƙararrawa yayin da shirye-shiryen zaɓen 2027 ke ɗaukar zafi.
“Ko Shugaba Tinubu bai taɓa neman wani kaso na tsarin APC ba. Buƙatar kashi 20 cikin 100 ta kasance abin da ya karya yarjejeniyar. Haka kuma, kujerar mataimakin shugaban ƙasa dama ba ta kan tebur ba, kuma ba a da hujjar tattauna batun 2031 a wannan lokaci,” in ji wata majiya mai ƙarfi da ta halarci tattaunawar.
A gefe guda, ɓangaren Dr. Boniface Aniebonam a NNPP ya ce ficewar Gwamna Abba Kabir Yusuf daga jam’iyyar ya samo asali ne daga halin danniya da yunƙurin Kwankwaso na iko da komai.
Har ila yau, mai ba Gwamna Yusuf shawara kan siyasa, Alhaji Mustapha Bakwana, ya ce a wani shirin rediyo na cikin gida cewa warware rikicin masarautar Kano muhimmin ginshiƙi ne ga ci gaban siyasar jihar. Ya ƙara da cewa gwamnati na shirin haɗa Masarautar Kano ƙarƙashin shugaba guda domin kawo ƙarshen ta ƙaddamar da ke ci gaba.
[ad_2]
Source link