Sojoji Sun Nemi Ƴan Sokoto Su Miƙa Ragowar Ɓaraguzan Bam Ɗin Amurka

[ad_1]

Bayan harin saman da rundunar Sojin Amurka ta kai a ranar Kirsimeti a Arewacin Nijeriya, hukumomin soja a Jihar Sokoto sun yi kira ga mazauna jihar da su mika duk wani ragowar bam ko wani ɓaraguzan fashe wa da suka samu daga wuraren harin. Wannan mataki na nufin kare haɗɗari da tabbatar da tsaron jama’a.

Harin saman, wanda aka kai daga daren 25 ga Disamba zuwa safiyar 26 ga Disamba, 2025, ya mayar da hankali ne kan sansanonin ƴan ta’adda masu alaƙa da ƙungiyar ISWAP a dajin Bauni. Harin, wanda rundunar Amurka da Nijeriya suka haɗa kai wajen kai wa, ya yi amfani da makaman da ake jagoranta ta na’urar sarrafawa (GPS) da jiragen sama marasa matuƙi don lalata cibiyoyin ƴan ta’adda a yankin Sahel.

  • Amurka Ta Yi Iƙirarin Kama Shugaban Ƙasar Venezuela
  • Amurka Ta Bayyana Dalilin Janye Jakadanta Daga Nijeriya Da Wasu Kasashe 29

A wani bayani da shalƙwatar tsaron Nijeriya ta fitar, an bayyana cewa harin ya dogara ne kan bayanan sirri kuma an sami nasarar kashe barazanar da akai nufi, ba tare da jikkata fararen hula ba. Ana ci gaba da tantance sakamakon harin, kuma ana sa ran ƙarin bayani daga hukumomi bayan kammala bincike.

Duk da tabbacin cewa babu farar hula da suka rasa rayuka, ragowar kayan fashe wa da abubuwan da ba a tantance ba da suka faɗo kusa da yankin sun haifar da damuwa kan tsaro. Sojojin sun yi kira ga mazauna yankin da su hanzarta miƙa duk wani ragowar bam ko kayan da suka ɗauka ga hukumomin tsaro don kauce wa fashewar haɗari da kuma taimakawa wajen cikakken bincike na ɓarnar da aka yi.

Haka kuma, an shawarci mazauna da su kai rahoton wuraren da ake zargin akwai kayan fashewa. Gwamnatin Jihar Sokoto ta tabbatar da harin kuma ta bayyana cewa aikin haɗin gwuiwa da rundunar Amurka wani ɓangare ne na ci gaba da ƙoƙarin kare rayuka da dukiyoyi daga barazanar ƴan ta’adda.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *