An sallami Anthony Joshua daga asibiti
[ad_1]
An sallami fitaccen ɗan wasan damben duniya, ɗan asalin Najeriya daga asibitin Duchess International Hospital da ke Ikeja, a Jihar Legas, bayan hatsarin mota da ya yi.
Hatsarin mota ya rutsa da Joshua a kan hanyar Legas zuwa Ibadan wanda ya yi sanadin rasuwar abokan aikinsa, Lateef Ayodele da Gami Cina.
Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Legas, Gbenga Omotoso, da Hadimin Gwamnan Ogun, Kayode Akinmade, sun tabbatar da cewa Joshua yana murmurewa a gida.
A cikin sanarwar, an ce Joshua da mahaifiyarsa sun je Legas don yin bankwana da waɗanda suka rasu kafin kai gawarwakin ga iyalansu.
Gwamnan Jihar, Babajide Sanwo-Olu, da na Ogun, Dapo Abiodun, sun gode wa jama’a bisa nuna damuwa da goyon baya.
Sun kuma gode wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma ƙungiyar likitoci a Lagoon Hospital, Ikoyi, bisa kulawa da ƙwarewar da suka nuna.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link