AFCON 2025: Super Eagles ta tsallaka zagayen ’yan 16
[ad_1]
Tawagar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles ta Najeriya, ta tsallaka zagayen ’yan 16, bayan doke ƙasar Tunusiya da ci 3 da 2.
Ƙasashen biyu daga rukunin C, sun ɓarje gumi da misalin ƙarfe 9 agogon Najeriya.
Wasan ya ɗauki hankali duba da yadda ƙasashen suka saba haɗuwa a gasar Nahiyar Afirka.
Wasan ya ƙayatar da kallo ganin yadda ƙasashen suka murza leda a daren ranar Asabar a ƙasar Maroko.
Fitaccen ɗan wasan gaban Najeriya da Galatasaray, Victor Osimhen ne, ya fara jefa ƙwallo a ragar Tunusiya a minti na 44.
Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Kyaftin ɗin Super Eagles, Wilfred Ndidi, ya sake sanya Najeriya a gaba a minti na 50.
A minti na 67 Ademola Lukman ya sake jefa wa Super Eagles ƙwallo ta uku a ragar Tunusiya.
A minti na 74 ne Tunusiya ta yi huɓɓasa ta hanyar jefa ƙwallo ta hannun ɗan wasanta, Talbi.
Shi kuwa Ali Abdi, ya jefa ƙwallonsa a minti na 87 daga bugun fenariti.
Najeriya ce ke jan ragamar teburin rukunin da maki 6 daga wasa biyu da ƙwallo biyar, yayin da aka jefa mata ƙwallo uku a raga.
Ita kuwa Tunusiya tana mataki na biyu a rukunin da maki 3, bayan lashe wasa ɗaya da rashin nasara ɗaya.
Tanzaniya tana mataki na uku, sai Uganda a mataki na ƙarshe, dukkaninsu da maki ɗaya-ɗaya, bayan rashin nasara da yin kunnen doki a wasanni biyu da suka buga.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link