AFCON 2025: Super Eagles ta tsallaka zagayen ’yan 16

[ad_1]



Tawagar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles ta Najeriya, ta tsallaka zagayen ’yan 16, bayan doke ƙasar Tunusiya da ci 3 da 2.

Ƙasashen biyu daga rukunin C, sun ɓarje gumi da misalin ƙarfe 9 agogon Najeriya.

Wasan ya ɗauki hankali duba da yadda ƙasashen suka saba haɗuwa a gasar Nahiyar Afirka.

Wasan ya ƙayatar da kallo ganin yadda ƙasashen suka murza leda a daren ranar Asabar a ƙasar Maroko.

Fitaccen ɗan wasan gaban Najeriya da Galatasaray, Victor Osimhen ne, ya fara jefa ƙwallo a ragar Tunusiya a minti na 44.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Kyaftin ɗin Super Eagles, Wilfred Ndidi, ya sake sanya Najeriya a gaba a minti na 50.

A minti na 67 Ademola Lukman ya sake jefa wa Super Eagles ƙwallo ta uku a ragar Tunusiya.

A minti na 74 ne Tunusiya ta yi huɓɓasa ta hanyar jefa ƙwallo ta hannun ɗan wasanta, Talbi.

Shi kuwa Ali Abdi, ya jefa ƙwallonsa a minti na 87 daga bugun fenariti.

Najeriya ce ke jan ragamar teburin rukunin da maki 6 daga wasa biyu da ƙwallo biyar, yayin da aka jefa mata ƙwallo uku a raga.

Ita kuwa Tunusiya tana mataki na biyu a rukunin da maki 3, bayan lashe wasa ɗaya da rashin nasara ɗaya.

Tanzaniya tana mataki na uku, sai Uganda a mataki na ƙarshe, dukkaninsu da maki ɗaya-ɗaya, bayan rashin nasara da yin kunnen doki a wasanni biyu da suka buga.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *