Sin Ta Dauki Matakin Mayar Da Martani Kan Sayar Da Makaman Amurka Ga Yankin Taiwan Na Kasarta
[ad_1]
Shafin intanet na ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya fitar da wani sako a yau Jumma’a 26 ga wata, inda ya bayyana cewa, a matsayin martani ga sabuwar sanarwar da Amurka ta fitar ta sayar da manyan makamai ga yankin Taiwan na kasar Sin, kasar ta Sin ta yanke shawarar daukar matakan da suka dace bisa dokar Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin game da tinkarar takunkumin kasashen waje, a kan kamfanoni 20 na Amurka da ke da alaka da sojan Amurka da kuma wasu shugabanni 10 na kamfanoni, wadanda suke da hannu dumu-dumu wajen samar da makamai ga Taiwan a ‘yan shekarun nan.
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya jaddada cewa, batun Taiwan yana sahun gaba a cikin manyan muradun kasar Sin, kuma kan iyaka ne da ya zama wajibi kada a tsallaka a huldar Sin da Amurka. Duk wanda ya yi yunkurin ketare iyakar da yin tsokana game da batun Taiwan, zai gamu da martanin kasar Sin. Sannan, duk wani kamfani ko mutumin da ke sayar da makamai ga Taiwan zai girbi abin da ya shuka. Babu wata kasa ko wani karfi da zai taba raina kuduri, da karfin ikon da gwamnati da jama’ar kasar Sin ke da su na kiyaye ‘yancin kai da kare martabar yankin kasar.
Mai magana da yawun ma’aikatar ya kuma bayyana cewa, kasar Sin ta sake yin kira ga Amurka da ta mutunta ka’idar Sin daya tilo a duniya da kuma sanarwar hadin gwiwa guda uku wadda Sin da Amurka suka fitar, da cika alwashin da shugaban Amurka ya dauka, da dakatar da yunkuri mai hatsari na bai wa Taiwan makamai, da dakatar da kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun Taiwan, da kuma dakatar da yi wa ‘yan awaren Taiwan ingiza mai kantu ruwa a kan “’yancin kan Taiwan”. Kasar Sin za ta ci gaba da daukar kwararan matakai don tabbatar da cikakken ikon kasarta, tsaro da kuma cikakken kare martabar yankinta. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
[ad_2]
Source link