Babban Hafsan sojojin Libya da wasu mutum 7 sun rasu a hatsarin jirgin sama a Turkiyya

[ad_1]



Babban Hafsan sojojin kasar Libya da wasu manyan hafsoshi hudu sun rasu a daren Talata lokacin da jirgin da suke ciki ya yi hatsari jim kaɗan bayan tashi daga Ankara babban birnin Turkiyya.

Hukumomi a Ankara da Tripoli babban birnin kasar ta Libya sun ce an gano ragowar jirgin na Falcon 50 ɗin da suke ciki ta hannun jami’an tsaron Turkiyya a yankin Haymana kusa da Ankara, in ji Ministan Cikin Gida na Turkiyya, Ali Yerlikaya.

Ƙarin ma’aikatan jirgin guda uku ma sun rasu.

Firaministan Libya, Abdulhamid Dbeibah, ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa: “Cikin bakin ciki da jimami muka samu labarin rasuwar shugaban hafsoshin sojojin Libya, Laftanar Janar Mohammed al-Haddad.”

A ranar Talata da safe, Haddad ya yi ganawa a Ankara da Ministan Tsaron Turkiyya, Yasar Guler, da takwaransa Selcuk Bayraktaroglu, sannan ya nufi Tripoli.

Yerlikaya ya bayyana a X cewa jirgin Haddad ya tashi daga filin jirgin Esenboga na Ankara da karfe 5:10 na yamma a agogon GMT, kuma “an rasa hulɗa da shi” bayan mintuna 42 da tashinsa.

Jirgin ya aika da sanarwar gaggawar sauka a Haymana mai nisan kilomita 74 daga Ankara, amma ba a sake samun hulɗa da shi ba, in ji ministan.

Wani babban jami’in Turkiyya ya ce jirgin ya nemi saukar gaggawa saboda matsalar lantarki bayan mintuna 16 da ya tashi.

Jirgin ya ɗauki fasinjoji takwas, ciki har da Haddad, hafsoshin soja hudu da ma’aikata uku. “Sun aika da sanarwar gaggawa ga cibiyar kula da zirga-zirgar jiragen sama saboda matsalar lantarki, suna neman saukar gaggawa,” in ji Burhanettin Duran, shugaban sashen sadarwar fadar shugaban ƙasa, a shafin X.

Ministan Shari’a na Turkiyya, Yilmaz Tunc, ya ce ofishin babban mai gabatar da ƙara na Ankara ya kaddamar da bincike kan lamarin.

Kafofin yada labarai na Turkiyya da dama sun nuna hotunan yadda sararin sama ta yi walƙiya da karar wata fashewa a kusa da inda jirgin ya aika da alama.

Burhan Cicek, wani mazaunin Haymana, ya tuna lokacin da jirgin ya yi hatsari.

“Na ji ƙarar fashewa mai ƙarfi. Kamar ta bam,” in ji shi ga AFP.

Jakadan Libya a Ankara ma ya halarci wurin.

Walid Ellafi, Ministan Sadarwa da Harkokin Siyasa na Libya, ya shaida wa tashar Libya al-Ahrar cewa gwamnatin Turkiyya ta sanar da su lamarin.

“Mun samu kira daga hukumomin Turkiyya cikin gaggawa bayan lamarin, suna cewa an rasa hulɗa da jirgin,” in ji ministan.

Ya ƙara da cewa duk hulɗa da jirgin ta ƙare kusan rabin sa’a bayan tashinsa daga filin jirgin Ankara saboda matsalar fasaha.

“Muna jiran sakamakon binciken Turkiyya, kuma alamu sun nuna jirgin ya yi hatsari ne,” in ji shi.

Ministan ya ce sauran mutanen da ke cikin jirgin sun haɗa da mai ba Haddad shawara, Mohammed Al-Assawi, da Janar Al-Fitouri Ghraibil, Janar Mohammed Jumaa, da mai rakiyarsu Mohammed Al-Mahjoub.

Haddad ya kasance shugaban hafsoshin sojojin Libya tun watan Agustan 2020, lokacin da tsohon Firaminista Fayez al-Sarraj ya naɗa shi.

Libya ta kasu gida biyu tsakanin gwamnatin da Majalisar Ɗinkin Duniya ta amince da ita a Tripoli ƙarƙashin Dbeibah, da kuma gwamnatin kwamanda Khalifa Haftar a gabashin kasar.

Ƙasar ta rabu tun bayan kifar da gwamnatin Moamer Ghaddafi da NATO ta tallafa a 2011.

Turkiyya na da kusanci da gwamnatin da Majalisar Dinkin Duniyar ta amince da ita a Tripoli, inda take ba ta tallafin tattalin arziki da soja, tare da yawan ziyara tsakanin bangarorin biyu.

AFP


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *