An Kaddamar Da Aikin Gyaran Babbar Hanyar Da Ta Hade Senegal Da Guinea-Bissau
[ad_1]
An gudanar da bikin kaddamar da aikin gyaran babbar hanyar Bissau zuwa Dakar, wadda kamfanin CHEC na kasar Sin zai aiwatar, kana ake sa ran bayan kammalarta za ta inganta harkokin sufuri tsakanin kasashen Senegal da Guinea-Bissau.
An yi bikin kaddamar da aikin ne jiya Litinin a garin Tanaff na kudancin kasar Senegal. Inda aka bayyana cewa, kason farko na babbar hanyar mai tsayin kilomita 26.4, zai tashi ne daga garin Tanaff zuwa kan iyakar Senegal da Guinea-Bissau.
A jawabinsa yayin bikin, shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye, ya ce inganta hanyar zai saukakawa ‘yan kasarsa zirga-zirga, da kara kyautata tafiye-tafiye tsakanin Senegal da Guinea-Bissau.
A nasa jawabin kuwa, mataimakin babban manajan kamfanin gine-gine na CHEC reshen yammacin Afirka Sun Haijun, cewa ya yi kamfaninsu zai gudanar da aikin hanyar bisa tsari mai inganci, da wa’adin da aka amince da shi, don tabbatar da aiwatar da shi yadda ya kamata, ta yadda zai amfani al’umma ta fuskar bunkasa tattalin arziki da zamantakewa. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
[ad_2]
Source link