’Yan Bindiga Sun Sace Matafiya 28 A Jihar Filato

[ad_1]

’Yan bindiga sun sace aƙalla matafiya 28 a daren ranar Lahadi a ƙauyen Zak da ke Ƙaramar Hukumar Wase ta Jihar Filato.

Wani shugaban matasa, Sapi’i Sambo, ya ce waɗanda aka sace sun haɗa da maza, mata da yara.

  • An Bullo Da Sabon Daftarin Dokar Kiyaye Muhallin Halittu Na Kasar Sin
  • AFCON 2025: Afirka Ta Kudu Ta Doke Angola Da Ci 2-1

Suna kan hanyarsu ne daga Zak zuwa Sabon Layi domin halartar bikin Mauludi lokacin da aka kai musu hari da misalin ƙarfe 8 na dare.

Ya ce maharan sun tare motar sannan suka tafi da dukkanin fasinjojin, suka bar motar a wajen.

Daga cikin waɗanda aka sace akwai ’ya’yan masu sauratar gargajiya biyu da kuma wani malamin addini.

An gano motar da aka bari da safiyar ranar Litinin, amma har yanzu ba a san inda aka kai mutanen ba.

An sanar da jami’an tsaro game da lamarin.

’Yansanda sun ce suna binciken faruwar lamarin.

Sace-sace da ayyukan ’yan bindiga sun yi ƙamari a yankin Wase.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *