‘Yan Ƙunar Baƙin Wake Sun Kashe Jami’ai 3 A Hedikwatar Rundunar Tsaro Ta Pakistan

[ad_1]


Akalla jami’an tsaro uku ne suka mutu a ranar Litinin bayan da ‘yan kunar bakin wake suka kai hari kan hedikwatar rundunar jami’an tsaro ta cikin gida (FC) da ke Peshawar, arewa maso yammacin Pakistan.

A cewar jami’an ‘yansanda da jami’an tsaro, maharan uku sun kusa kutsawa cikin harabar hedikwatar yayin da ɗaya daga cikinsu ya tayar da bam a bakin kofar, sauran kuma suka yi yunkurin kutsa da karfi.

Jami’an tsaro sun yi gaggawar harbe su, inda suka hana maharan shiga cikin sansanin.

Fashewa bam da harbe-harben da suka biyo baya sun yi sanadiyyar mutuwar ma’aikatan FC uku tare da jikkata wasu akalla biyar, in ji hukumomin tsaron kasar.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *