DSS ta gurfanar da matashin da ya yi kira a yi juyin mulki a Najeriya a gaban kotu

[ad_1]



Hukumar tsaro ta DSS ta gurfanar wani matashi mai suna Innocent Chukwuemeka Onukwume, mai shekaru 27, bisa zargin kiran sojoji da su yi juyin mulki a Najeriya.

Hukumar dai ta shigar da ƙarar matashin ne cikin tuhuma shida a gaban Kotun Tarayya da ke Abuja.

An shigar da ƙarar ne mai lamba FHC/ABJ/CR/610/2025, dangane da wasu rubuce-rubuce da matashin ya wallafa a shafinsa na X a watan Oktoban 2025.

A cewar DSS, waɗannan rubuce-rubuce sun nemi a kifar da gwamnatin jam’iyyar APC mai mulki tare da nuna goyon baya ga sojoji su karɓi mulki a ƙasar.

Lauyan DSS, A.M. Danalami, ya shigar da ƙarar a ranar Talata, inda aka bayyana cewa ayyukan wanda ake zargin sun saɓa da sashe na 46A(1) da 59(1) na Dokar Manyan Laifuka ta Ƙasa, da kuma Sashe na 24(1)(b) na Dokar Laifukan Intanet ta 2024 (wacce aka yi wa gyara).

Daga cikin kalaman da ake zargin ya wallafa akwai: “Ana buƙatar juyin mulki a Najeriya. A kawar da APC, a dakatar da gwamnatin Najeriya, a shiga kungiyar AES. Wannan ne kawai muke buƙata yanzu.”

Haka kuma, ana zargin ya rubuta cewa: “A karshe zai faru,  yak u ’yan Najeriya. Sojoji na buƙatar goyon bayanku yanzu! Su kaɗai ne za su iya ceton ƙasar nan. Wanda ke Aso Rock ya sayar da ƙasar nan ga Turawa, su ke sarrafa sirrikanmu. Sojoji kaɗai za su iya sake daidaita ƙasar nan.”

A wani rubutu daban kuma ya ce: “Dole ne Tinubu ya tafi, kuma dole APC ta mutu kafin Najeriya ta samu daidaito.”

Ana sa ran za a gurfanar da Onukwume, wanda mazaunin Umusayo Layout ne a Karamar Hukumar Oyigbo ta Jihar Ribas a kotu cikin makon nan.

A watan Oktoba, an samu rahotanni da ke nuna cewa wasu jami’an sojoji sun yi yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *