Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro



Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance Kingsley Udeh (SAN), wanda Shugaba Bola Tinubu ya zaɓa domin zama minista daga Jihar Enugu, saboda rashin samun takardar tantancewa daga hukumomin tsaro.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana a zaman majalisar na ranar Laraba cewa ba za a ci gaba da tantance Udeh ba sai ya samo rahoton tsaro da ake buƙata.

Ya ce, “Tantancewar wanda aka ba da shawarar a yi masa naɗin minista ta kamata ta biyo baya, amma muna buƙatar takardar tsaro kafin hakan.”

Shugaba Tinubu ya tura sunan Udeh zuwa majalisar domin maye gurbin Uche Nnaji, tsohon Ministan Ƙirƙire-ƙirƙire, Kimiyya da Fasaha, wanda ya yi murabus a watan da ya gabata saboda rikicin da ya taso kan takardun karatunsa.

Murabus ɗinsa ya sa Jihar Enugu ba ta wakilci a Majalisar Zartarwa ta Tarayya.

Akpabio ya mayar da martani cewa ba su da niyyar ɓata lokaci, inda ya ce, “Ba zan jira kowa ba, saboda da zarar an tantance su, ba za a sake ganinsu ba.”

Daga nan sai ‘yan majalisar suka shiga zaman sirri domin tattauna batutuwan da suka shafi ƙasa.



Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *