Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

[ad_1]

Ƴar wasan gaba ta tawagar Super Falcons ta Nijeriya, Ifeoma Onumonu, ta sanar da yin ritaya daga buga ƙwallon kafa a ranar Asabar, ta hanyar wallafa saƙo a shafinta na Instagram.

Onumonu ta bayyana cewa lokacin ya yi da za ta rataye takalmanta, domin ba wa matasa masu tasowa dama su nuna bajintarsu a filin wasa. Sai dai ta ce ritayarta ba ta nufin cewa za ta bar harkokin ƙwallon ƙafa gaba ɗaya.

A tsawon shekaru fiye da 20, Onumonu ta bar tarihi mai kyau a fagen ƙwallon ƙafa, inda ta samu nasarori da dama tare da Super Falcons, ciki har da buga gasar Kofin Duniya, da kuma lashe Kofin ƙasashen Afrika ta Mata (WAFCON) a watan Yuni 2024.

Onumonu mai shekaru 31, ta rubuta cewa:

Cike godiya a zuciya, nake yin bankwana da taka leda a filin wasa. “

Kafin ta wakilci Nijeriya, Onumonu ta fara buga wasa ne da ƙungiyar ƴan ƙasa da shekaru 23 ta Amurka, kafin ta sauya ra’ayi zuwa ƙasarta ta asali.

A matakin ƙarshe na buga ƙwallonta, Onumonu ta taka leda a kulob ɗin Montpellier na ƙasar Faransa, kafin ta yanke shawarar yin ritaya.

Ta kuma bayyana cewa tana da niyyar ci gaba da aiki a fagen kwallon kafa, ko a matsayin mai horarwa ko kuma mai ba da shawara, inda ta ce:

“Zan yi amfani da ƙwarewar da Allah ya bani wajen taimaka wa ƙungiyoyin ƙwallon kafa a Nijeriya.”




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *