Manchester United za ta ɗauki golan Antwerp, Senne Lammens

[ad_1]



Manchester United ta amince za ta ɗauki golan tawagar Belgium, Senne Lammens daga Royal Antwerp kan fam miliyan 18.1 har da karin tsarabe-tsarabe.

Sasashen wasanni na BBC ya ruwaito cewa hakan ya kawo karshen zawarcin golan Aston Villa, Emiliano Martinez da ta yi.

Lammens, mai shekara 23, zai saka hannu a ƙungiyar Old Trafford kan yarjejeniyar kaka biyar.

United na fatan ɗinke ɓarakar gurbin mai tsaron raga, bayan da Altay Bayindir ke kuskure a wasannin Firimiya, yayin da ake zargin Andre Onana da sakacin da ya janyo aka fitar da United a Carabao Cup a hannun Grimsby.

Lammens ya koma Antwerp a matakin mara ƙunshin yarjejeniya daga Club Brugge a 2023, wanda ya tsare raga karo 64 a Antwerp da lashe Belgian Super Cup a 2023.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *