FIFA ta ce za a gudanar da Gasar Kofin Duniya duk da rikicin Iran

[ad_1]



Hukumar ƙwallon ƙafa ta duniya FIFA ta jaddada cewa za a ci gaba da shirye-shiryen gudanar da Gasar Kofin Duniya ta 2026 kamar yadda aka tsara, duk da rashin tabbas kan halartar Iran.

Shugaban FIFA, Gianni Infantino ne ya bayyana hakan a yayin taron majalisar hukumar da aka gudanar ta yanar gizo, inda ya ce hukumar na sa ran dukkan ƙasashe 48 za su halarci gasar cikin adalci da mutunta juna.

Sai dai halartar Iran na fuskantar shakku sakamakon yaƙin da ke gudana a Gabas ta Tsakiya, musamman rikicin da ya shafi Amurka da Isra’ila.

Shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta Iran, Mehdi Taj, ya nuna cewa ƙasar na shirin halartar gasar, amma tana son a sauya wuraren wasanninta daga Amurka zuwa sauran ƙasashen da za su karɓi bakuncin gasar, wato Canada ko Mexico.

Ya ce Iran na iya ƙaurace wa buga wasa a Amurka, amma ba za ta janye daga gasar baki ɗaya ba.

Haka kuma, shugabar ƙasar Mexico, Claudia Sheinbaum, ta bayyana cewa ƙasarta a shirye take ta karɓi baƙuncin wasannin Iran idan buƙatar hakan ta taso.

Infantino ya ƙara da cewa duk da cewa FIFA ba za ta iya warware rikice-rikicen siyasar duniya ba, amma tana fatan amfani da ƙwallon ƙafa wajen haɗa kan al’umma da inganta zaman lafiya.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *