An gargaɗi jama’a su yi aiki tare da hukumomin tsaro a Yobe

[ad_1]



Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe ta nuna matuƙar tausayawa ga gwamnati da al’ummar Maiduguri, jihar Borno, bayan afkuwar fashewar bama-bamai da suka faru a ranar 16 ga Maris, 2026, da misalin ƙarfe 18:30 a wurare daban-daban a cikin Maiduguri.

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP Dungus Abdulkareema a ranar Talata 17 ga Maris 2026 ya fitar ya ce, rundunar ta yi kira ga mazauna jihar Yobe da su kwantar da hankalinsu, su yi taka-tsantsan, kuma su kasance cikin tsaro, musamman a ciki da kewayen al’ummominsu, wuraren jama’a da sauran wurare masu cunkoso.

Bayan taron majalisar tsaron Jiha da aka gudanar a fadar gwamnatin Jihar Yobe a ranar 16 ga Maris, 2026, wanda ya shafi dukkan hukumomin tsaro a jihar, an sanya tsauraran matakan tsaro a faɗin jihar kafin bukukuwan Sallah mai zuwa kamar yadda tun farko gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni ya bada umarni akan hakan.

Kwamishinan ‘Yan Sanda, Emmanuel Ado, psc, fdc, ya umarci Kwamandojin yankuna, Jami’an ‘yan Sanda na Sashe, Sashen dabaru, da sashen leƙen asiri da su tabbatar da tsaro mai inganci a cibiyoyin ibada, wuraren shaƙatawa na jama’a, da sauran wurare masu muhimmanci kafin, lokacin da kuma bayan bukukuwan Sallah.

Ana ƙarfafawa jama’a da su yi aiki tare da hukumomin tsaro ta hanyar samar da sahihan bayanai game da harkokin mutane, motoci ko babura da ake zargi zuwa ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

Ana kuma gargaɗin masu ababen hawa da sauran masu amfani da hanya da su guji tuƙi ba tare da kulawa ba da kan haifar da haɗari a lokacin bukukuwan domin tabbatar da tsaron jama’a.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *