Gwamnatin Kwara Za Ta Gyara Makarantu 898

[ad_1]

Gwamnatin Jihar Kwara za ta gyara manya da kananan Makarantu 898  domin tabbatar da za’a  samar da ilimi mai nagarta.

Gwanbatin Jihar ta kaddamar da kwamiti mai samar da fasaha (TSPs) a karkashin tsarin kula da ‘yanmata da suke  a tsakanin shekarun 10, 18, da 24,na taimaka masu ta bangaren ilimi da kuma yadda za su dogara da kansu ( AGILE).

  • Nijeriya Na Yunkurin Mayar Wa Da Manoman Tumatir Asarar Da Suka Yi Ta Naira Biliyan 1.3
  • Arsenal Na Tattaunawa Da Declan Rice Kan Tsawaita Kwantiraginsa A Ƙungiyar

Kwamishinan ilimi da ci gaban al’umma, Dokta. Lawal Olohungbebe,shi ne ya kaddamar da horon na kwana biyu ga mambobin kwamitin.

Olohungbebe ya jinjinawa  Gwamna AbdulRahman AbdulRazak ta yadda ya maida hankalin sa da  kuma kulawa da abinda zai taimakawa rayuwa domin bunkasa tattalin arziki da ilimi na al’umma, ta hanyar maida hankali akan wasu mutanen da suke bukatar saboda halin da suke ciki na fatara, za kuma a iya cutar da su ko gallaza masu,suna fuskantar rashin tsaftam da dai wadansu abubuwan da suka sa ba za su iya yin wani abu ba.Irin wadannan sau da yawa ana nuna masu wariya ga kuma kuntata masu idan wata bukata ta taso, bama kamar idan abin ya zama tilas ne sai an same shi.Wadannan mutane sun hada da yara, tsofaffi, mutane masu bukata ta musamman,‘yan gudun Hijirar,da kuma wadanda kabilarsu bata da yawa.

Duk da hakan jami’in da yake kula da shirin AGILE na Jihar Kwara, Mista Adeshina Salami, ya bayyana muhimmanci  da irin hadin kai da ganin mutuncin juna da ke tsakanin kwamitin  makaranta da kuma masu samar da fasaha a tabbatar da an samu nasara.

Ya bada tabbacin cewar duk makarantu za su amfana da tanadin samar da tsaftataccen ruwa, kulawa da muhalli da duk abubuwan da aka san za su taimaka ga cimma shi tsarin na (WASH).

Ita jami’ar kulawa da muhalli ta kasa mai kulawa da Abuja (NPCU), Mrs. Nkechi Ikemefuna cewa ta yi shi horon, yana da matukar miuhimmanci domin yana taimakawa wajen ganewa,  ta yadda za’a hana aukuwar matsalar da za’a iya fuskanta data shafi muhalli da kuma abinda ka iya shafar zamantakewa ta al’umma bama kamar idan bukatar tsugunnar da mutane zuwa wani wuri idan bukatar hakan ta taso.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *