Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin hare-hare a Iran

[ad_1]



Ƙasar Isra’ila ta sanar da ƙaddamar da wani sabon hari na gargaɗi kan Iran a ranar Asabar, kamar yadda Ministan Tsaron ƙasar, Israel Katz, ya bayyana.

A cikin wata sanarwa, ma’aikatar tsaron Isra’ila ta ce ta kai harin ne a matsayin “hari na rigakafi” domin kawar da wata babbar barazana, inda aka ayyana dokar ta-ɓaci ta musamman a faɗin ƙasar.

Hakan ya biyo bayan ƙarar ƙararrawar gargaɗi a Jerusalem, tare da saƙonnin gargaɗi da aka tura wa jama’a ta wayar salula game da abin da aka kira “mummunar barazana”.

Rahotanni daga Iran sun ce an ji ƙarar fashewar bama-bamai da dama a babban birnin ƙasar, Tehran, a ranar Asabar.

Sai dai har zuwa yanzu, ba a tabbatar da takamaiman wuraren da aka kai wa hare-haren ba, kuma hukumomi ba su fitar da bayanan asarar rayuka ko raunuka ba.

Wasu rahotanni sun nuna cewa ɗaya daga cikin hare-haren ya shafi wani yanki kusa da ofisoshin Jagoran Ƙoli na Addini a Iran, Ayatollah Ali Khamenei.

Ministan Sufuri, Miri Regev, ta bayar da umarnin rufe sararin samaniyar ƙasar baki ɗaya ga jiragen farar hula, a wani yunƙuri na ɗaukar mataki a sakamakon sabon yanayin tsaron da ya taso.

Har yanzu dai ana ci gaba da sa-ido kan lamarin, yayin da ƙasashen duniya ke nuna damuwa kan yiwuwar faɗaɗar rikicin da ke ƙara ƙamari tsakanin Isra’ila da Iran.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *