2027: Gwamna Ododo Ya Shirya Gangamin Goyon Bayan Tinubu A Kogi
[ad_1]
Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Ahmed Usman Ododo, ya buƙaci al’ummar ƙaramar hukumar Kogi da su haɗa kai wajen mara wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu baya gabanin zaɓen 2027, yana mai cewa ci gaba da goyon bayan shugaban ƙasa zai taimaka wajen ƙarfafa gyare-gyaren tattalin arziƙi da kuma tabbatar da ci gaban ƙasa na dogon lokaci.
Ododo ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar godiya da ya kai Kotokarfe a ranar Lahadi, inda ya kuma duba ayyukan raya ƙasa da ake yi a yankin, yana mai jaddada cewa ci gaba da jagoranci iri ɗaya a matakin tarayya zai tabbatar da ɗorewar manufofin da aka fara aiwatarwa tare da samar da ƙarin alfanun dimokuraɗiyya ga al’umma.
- 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya
- Farfadowar Halittun Ruwa A Kogin Yangtze Ta Nuna Kyakkyawan Yanayi
Ya yabawa Shugaba Tinubu kan manufofinsa da ya ce suna da hangen nesa duk da wahalhalun da ke tattare da su, yana mai cewa matakan da ake ɗauka yanzu za su haifar da daidaiton tattalin arziƙi a nan gaba, musamman ta fuskar inganta ababen more rayuwa kamar aikin gyaran hanyar Lokoja zuwa Abuja, wanda ya ce alama ce ta ƙudirin gwamnati wajen haɗa ƙasa da inganta sufuri.
Gwamnan ya kuma nuna godiya ga Sarkin Koto-Karfi, Ohimege Igu, Dakta Seidu Akawu Salihu da al’ummar yankin bisa goyon bayan da suke bai wa gwamnati, tare da jaddada cewa haɗin kai tsakanin jama’a da shugabanni shi ne ginshiƙin samun nasara a fannin tsaro da ci gaba mai ɗorewa a jihar.
A ƙarshe, Ododo ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta samar da dama iri ɗaya ga duk masu neman kujeru ba tare da tilas ta wa ba, yana mai cewa ikon zaɓen shugabanni yana hannun jama’a ne kawai, tare da kira ga ‘yan siyasa da su kusanci al’umma domin samun amincewarsu, domin shugabanci na gaskiya yana ginuwa ne kan hidima da yardar jama’a.
[ad_2]
Source link