‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara
[ad_1]
Jami’an ‘Yansandan Jihar Kwara sun ceto wani wanda aka yi garkuwa da shi, mai suna Haruna Ahmadu, daga maɓoyar masu garkuwa da mutane a wani daji da ke Omu-Aran, hedikwatar karamar hukumar Irepodun ta Jihar.
‘Yansandan sun kuma kama wasu mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, Ayisa Ibrahim da Yakubu Hassan a yankin.
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, Toun Ejire-Adeyemi, wanda ya sanar da wannan nasarar a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, ya ce ana ci gaba da kokarin kama sauran da suka tsere a yayin samamen a maɓoyarsu.
[ad_2]
Source link