’Yan sanda sun kama ɗan bindiga, sun ceto mutum 2 da aka sace a Nasarawa

[ad_1]



Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa, ta ceto mutum biyu da aka sace tare da kama wani mutum da ake zargin ɗan bindiga ne a jihar.

Kakakin rundunar, SP Ramhan Nansel, ya ce a ranar 3 ga watan Fabrairu, 2026, ’yan sanda sun ceto David O. daga Tudun Amba a Lafia.

David ya hau babur daga Lafia zuwa Assakio, amma direban babur ɗin ya sauya hanya zuwa cikin daji a ƙauyen Kireyi.

Wanda ake zargi ya tsere, kuma ’yan sanda na nemansa ruwa a jallo.

A wani labarin kuma, ’yan sanda sun kama Jamilu Salisu bisa zargin sace wani ɗalibi ɗan shekaru 14 a kusa da wani masallaci a Gitata.

An ceto yaron, amma wani abokin aikin nasa ya tsere.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Shetima Jauro Mohammed, ya bayar da umarnin a tsananta neman waɗanda suka tsere domin gurfanar da su s kotu.

Ya kuma gode wa al’ummar jihar kan haɗin kai, inda ya sake tabbatar da ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da tsaro a jihar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *