Tinubu zai kara yawan bashin da ake bin Najeriya zuwa Naira tiriliyan 195

[ad_1]



Bashin da ake bin Najeriya zai karu zuwa fiye da Naira tiriliyan 195 bayan da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya samu sahalewar Majalisar Dokoki ta Kasa na karbo sabon rancen Dala biliyan shida daga kasashen waje.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ke nuna damuwa kan yawan bashin da ƙasashe masu ƙaramin ƙarfin tattalin arziki ke fama da shi.

Aminiya ta ruwaito cewa a cikin wasiku biyu da ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Shugaban Majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, Tinubu ya bayyana cewa sabbin rancen za a yi amfani da su wajen aiwatar da ayyukan gine-gine, biyan bashi da kuma gyaran tashoshin jiragen ruwa.

A cewar wasikun wadanda aka amince da su a ranar Talata, sabbin rancen za su ƙara yawan bashin Najeriya daga Dala biliyan 110.3 zuwa dala biliyan 115.3.

Abin da za a yi da sabon bashin Dala biliyan shida

Shugaban Ƙasa ya roƙi majalisar da ta ba da “amincewa cikin gaggawa,” inda ya bayyana cewa za a yi amfani da takardun kuɗin Naira a matsayin jingina ga rancen.

A daya daga cikin wasikun, Shugaban Ƙasa ya nemi karbo rancen Dala biliyan 5 daga bankin First Abu Dhabi Bank da ke Ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE).

Shugaban Kasa ya roƙi majalisar da ta ba da “amincewa cikin gaggawa,” inda ya bayyana cewa za a yi amfani da takardun kuɗin Naira a matsayin jingina.

A daya wasikar kuma, yana neman karbo rancen Dala biliyan 1 daga Citibank London tare da tallafin UK Export Finance (UKEF), domin sabunta tashoshin jiragen ruwa na Lagos Port Complex da na Tin Can Islandda nufin inganta aiki, tsaro da inganci.

Ya bayyana cewa aikin gyaran zai magance matsalolin da suka daɗe suna damun tashoshin, ya ƙara tsaro da bin ƙa’idojin duniya, tare da tallafawa ci gaban tattalin arzikin ƙasa.

A cewarsa, rancen zai kasance da wa’adin biyan bashin shekaru 14, ciki har da karin wa’adin watanni 48 na samun damar amfani da kuɗin. Haka kuma akwai kuɗin “availability fee” na kashi 1.1% da kuma “UKEF premium” na kashi 1.07%.

Tun da farko, shugaban kwamitin majalisar dattawa kan rancen waje da na cikin gida, Sanata Wamakko Magatarkada Aliyu (Sokoto North), ya bayyana cewa kwamitin ya yi nazari sosai kan bukatar rancen kafin ya gabatar da rahoton sa a gaban majalisa domin amincewa.

Masana sun nuna damuwa

Rahoton Hukumar Kula da Basuka na Kasa (DMO) ya nuna cewa zuwa ranar 30 ga Satumba, 2025, jimillar bashin da ake bin Najeriya ya ƙaru zuwa Naira tiriliyan 153.29 (dala biliyan 103.94), sakamakon karo ciyo bashin cikin gida da na waje.

Wannan ya nuna an samu ƙaruwa daga Naira tiriliyan 152.40 da aka ruwaito a watan Yuni, 2025, inda bashin ya ƙunshi Naira tiriliyan 81.82 na cikin gida da kuma Dala biliyan 48.46 daga ketare.

Kodayake rahoton ƙarshe na 2025 bai fito ba tukuna, an yi hasashen cewa bashin zai iya haura Naira tiriliyan 189. Sabbin rancen da aka nema, idan aka juya su zuwa Naira, za su kai kimanin Naira tiriliyan 8.3 a kan farashin canjin kuxi na yanzu.

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya yi hasashen cewa jimillar bashin gwamnati ya kai kashi 34 bisa 100 na yawan kayan da ake samarwa a cikin gida, yayin da ake sa ran ajiyar kuɗin waje zai ƙaru zuwa Dala biliyan 51 a rahoton hasashen tattalin arzikin 2026.

“Ana hasashen bashin jama’a zai kai kashi 34.68 cikin 100 na GDP a ƙarshen 2026, idan aka kwatanta da kashi 33.98 cikin 100 a watan Yuni 2025, bisa sabbin rancen da ake sa ran za a ɗauka,” in ji rahoton.

Tattalin arziki na cikin haɗari —Dattawan Arewa

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta yi kira ga ’yan Najeriya da su yi magana kan abin da ta kira “yawan ciyo bashi mara tsari da kuma mai haɗari” da Gwamnatin Tarayya ke yi, tana gargadin cewa makomar tattalin arzikin ƙasa na cikin haɗari.

A wata wasika da ta aike wa ’yan ƙasa, NEF ta ce shiru a kan yawan bashin ya zama tamkar amincewa, tana mai jaddada cewa abin da ake fuskanta ba kawai shawarar kuxi ba ce, illa tsarin ciyo bashi da ke nuna raunin bin doka da rashin adalci.

Sanarwar da mai magana da yawun NEF, Farfesa Abubakar Jika Jiddere, ya sanya hannu, ta nuna damuwa kan rahoton cewa gwamnati na shirin neman qarin Naira tiriliyan 17.89 domin cike gibin kasafin 2026.

IMF ta nuna damuwa

Wani rahoto da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya fitar a ranar Talata taken Ci gaban Macroeconomic da Haɓaka a cikin Ƙasashe Masu Ƙasashe-2026, ya nuna damuwa kan ƙaruwar bashin cikin gida, tana mai cewa hakan na ƙara haifar da sabbin matsaloli ga ƙasashe masu ƙaramin ƙarfin tattalin arziki (LICs).

Rahoton ya bayyana cewa tattalin arzikin ƙasashen LICs—guda 70 da suka cancanci tallafin rage talauci da samar da ci-gaba—na fuskantar rashin tabbas daga sauyin manufofi a manyan ƙasashe,  ciki har da harkokin kasuwanci, ƙaura, kuɗin dijital, da tsare-tsaren kashe kuɗi, da kuma raguwar tallafin ƙasashen waje.

Duk da rage wasu matsalolin kuɗi a cikin shekaru, bashin jama’a ya ci gaba da zama barazana, musamman ga ƙasashen da ba su da isasshen ajiyar kuɗin waje.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *