Tankar Mai Ta Yi Mummunan Hatsari A Kogi, Gwamnati Ta Ɗauki Mataki
[ad_1]
Gwamnatin Jihar Kogi ta bayyana alhini kan mummunar hatsarin motar da ya afku a Unguwar Okunchi a Ƙaramar Hukumar Adavi. Ta kuma jaddada cewa za ta tallafa wa iyalan da abin ya shafa.
Wata tawaga ƙarƙashin jagorancin Alhaji Ahmed Tijani Oricha ta ziyarci yankin. Tawagar ta wakilci Gwamna Ahmed Usman Ododo domin jajanta wa al’umma da duba halin da ake ciki.
- Jihar Kogi Ta Ƙaddamar Da Masu Ba Da Taimakon Fasaha
- EFCC Ta Gabatar Da Ƙarin Hujjoji A Shari’ar Tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello
Hatsarin ya faru ne tsakanin tankar diesel da motar BUA Cement, inda gobara mai tsanani ta tashi. Wutar ta ƙone mutanen da ke cikin tankar gaba ɗaya ba tare da a gane su ba.
Haka kuma gobarar ta lalata wata gida da masallaci, duk da cewa babu asarar rai a waɗannan wuraren. A wani lamari kuma, wata mota mai ɗauke da fasinja biyu ta gamu da hatsari sakamakon zubewar diesel.
Mijin ya rasu nan take bayan ya rasa iko da babur ɗinsa, yayin da matar sa ke jinya a asibiti. Daga baya kuma direban motar BUA ya rasu bayan an kai shi asibiti, yayin da mataimakinsa ya tsira da rauni.
Al’umma da shugabannin yankin sun yaba da saurin martanin gwamnati. Sun jaddada cewa an yi amfani da kayan aiki wajen share wurin da kuma rage yawan ɓarnar.
Oricha ya bayyana cewa gwamnatin jihar za ta ƙara inganta hanyoyi da tsauraran matakan tsaro. Ya kuma tabbatar da jajen gwamnati ga iyalan waɗanda suka rasu.
[ad_2]
Source link