Shettima ya dawo Najeriya bayan halartar taro a Guinea da Switzerland
[ad_1]
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya dawo Abuja bayan shafe mako guda yana ziyarar aiki a ƙasashen Guinea da Switzerland.
Shettima, ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da Shugaban Ƙasar Guinea, Mamadi Doumbouya.
Daga nan kuma ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron Tattalin Arziƙin Duniya (WEF) karo na 56 da aka gudanar a birnin Davos na ƙasar Switzerland.
Bayan dawowa gida, Shettima ya ce Najeriya ta samu matsayi a tattaunawar siyasa da tattalin arziƙi a duniya.
A Guinea, ziyararsa ta mayar da hankali ne kan ƙarfafa rawar jagorancin Najeriya a Yammacin Afirka da kuma bunƙasa haɗin gwiwa a ɓangarorin noma da masana’antu.
A Davos kuwa, ya jagoranci tattaunawa da masu zuba jari, tare da ƙaddamar da ginin ‘Nigeria House Davos’, cibiyar da za ta riƙa tallata damar zuba jari a harkokin noma, albarkatun ƙasa da tattalin arziƙin zamani.
Shettima, ya kuma bayyana cewa tattalin arziƙin Najeriya na samun tagomashi, inda ake sa ran samun bunƙasar tattalin arziƙi a shekarar 2026.
Har ila yau, ana sa ran samun ragin hauhawar farashi, bunƙasa tsaron abinci, da kuma shirin ƙasar na zama babbar mai fitar da man fetur da aka tace.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link