Shettima ya dawo Najeriya bayan halartar taro a Guinea da Switzerland

[ad_1]



Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya dawo Abuja bayan shafe mako guda yana ziyarar aiki a ƙasashen Guinea da Switzerland.

Shettima, ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bikin rantsar da Shugaban Ƙasar Guinea, Mamadi Doumbouya.

Daga nan kuma ya jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron Tattalin Arziƙin Duniya (WEF) karo na 56 da aka gudanar a birnin Davos na ƙasar Switzerland.

Bayan dawowa gida, Shettima ya ce Najeriya ta samu matsayi a tattaunawar siyasa da tattalin arziƙi a duniya.

A Guinea, ziyararsa ta mayar da hankali ne kan ƙarfafa rawar jagorancin Najeriya a Yammacin Afirka da kuma bunƙasa haɗin gwiwa a ɓangarorin noma da masana’antu.

A Davos kuwa, ya jagoranci tattaunawa da masu zuba jari, tare da ƙaddamar da ginin ‘Nigeria House Davos’, cibiyar da za ta riƙa tallata damar zuba jari a harkokin noma, albarkatun ƙasa da tattalin arziƙin zamani.

Shettima, ya kuma bayyana cewa tattalin arziƙin Najeriya na samun tagomashi, inda ake sa ran samun bunƙasar tattalin arziƙi a shekarar 2026.

Har ila yau, ana sa ran samun ragin hauhawar farashi, bunƙasa tsaron abinci, da kuma shirin ƙasar na zama babbar mai fitar da man fetur da aka tace.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *