Sabuwar Yarjejeniyar FGN-ASUU: Tinubu Ya Amince Da Ƙarin Sabon Alawus Ga Farfesoshi

[ad_1]

Gwamnatin Tarayya ta fara aiwatar da sabuwar yarjejeniyarta da Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), inda Shugaba Bola Tinubu ya amince da ingantattun tsare-tsaren jin dadin malaman, gami da sabon alawus na wata-wata wanda zai sa Farfesoshin Jami’o’i su sami sama da Naira 140,000 a matsayin ƙarin albashi.

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya bayyana hakan a daren Laraba yayin da yake magana a shirin ‘Politics Today’ a gidan talabijin na Channels, yana mai jaddada cewa, yarjejeniyar za ta ɗore kuma an riga an fara aiwatar da ita.

A cewar Alausa, Shugaban ya amince da yarjejeniyar ne bayan ya tabbatar da cewa akwai isassun kudade, yana mai jaddada cewa Tinubu ba ya yin alkawuran da ba za a iya cikawa ba.

Alausa ya tabbatar da cewa, Gwamnatin Tarayya yanzu tana da albarkatun da za ta iya samar da ƙarin kashi 40 cikin 100 na albashi ga malamai a dukkan manyan makarantu, tare da cika sauran alƙawura guda tara waɗanda aka tsara acikin sabuwar yarjejeniya a fili.

A wani mataki da aka bayyana a matsayin wanda ba a taɓa ganin irinsa ba, Shugaban ya kuma amince da wani sabon nau’in alawus na Farfesoshi da sauran manya a ɓangaren ilimi.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *