Peng Liyuan Ta Yi Hira Da Uwargidan Shugaban Koriya Ta Kudu

[ad_1]

Peng Liyuan, uwargidan shugaban kasar Sin Xi Jinping, ta yi hira da Kim Hea Kyung, uwargidan shugaban kasar Koriya ta Kudu Lee Jae Myung, a birnin Beijing yau Litinin.

Peng ta yi maraba da Kim, wadda ta raka shugaba Lee a ziyararsa ta farko zuwa kasar Sin a farkon sabuwar shekara.

Da take bayyana cewa mabudin dangantaka a tsakanin kasa da kasa ya ta’allaka ne da zumunci na kusa a tsakanin mutane, Peng ta yi fatan cewa mutanen kasar Sin da Koriya ta Kudu a matsayin makwabta na kusa, za su kara fahimtar juna ta hanyar gudanar da cudanya a-kai-a-kai. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *