NDLEA ta kama matashi da wiwi ta miliyan 10 a Kano

[ad_1]



Hukumar NDLEA ta ce ta kama wani matashi mai suna Umar Adamu-Umar ɗauke da tabar wiwi mai nauyin kilo tara, wadda darajarta ta kai Naira miliyan 10 a Jihar Kano.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar ranar Asabar, ta ce ta cafke matashin mai shekara 27 ne a ranar 6 ga watan Agusta.

Hukumar ta kama shi ne a kan hanyar Kano zuwa Zariya, yana shirin safarar ƙunshi 19 na tabar wiwi daga Legas zuwa Kano.

Mai magana da yawun hukumar, Sadiq Muhammad-Maigatari, ya ce matashin ya amsa cewa shi ne yake safarar wiwin.

Kuma ya ce tun kafin a kama shi hukumar ta kwana biyu tana bin diddigin.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *