Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

[ad_1]

Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano ta kama wani matashi mai shekaru 30, mai suna Mutawakilu Ibrahim, bisa zargin caka wa kakanninsa wuƙa har sai da suka mutu bayan rigima a kan abinci.

Waɗanda abin ya rutsa da su su ne Muhammad Dansokoto mai shekaru 75 da Hadiza Tasidi mai shekaru 65, inda lamarin ya faru a gidansu dake unguwar Kofar Dawanau, da misalin ƙarfe 9:30 na safiyar ranar Alhamis, 25 ga watan Satumba, 2025.

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Kiyawa, ya bayyana cewa Ibrahim ya caka musu wuƙa a wurare da dama na jikinsu, lamarin da ya janyo musu mummunan rauni.

An garzaya da su asibitin Kwararru na Murtala Muhammad, inda aka tabbatar da mutuwarsu.

Daga baya an miƙa gawarwakin ga ‘yan uwansu domin yi musu sutura.

‘Yansanda sun ce wanda ake zargin yana cikin maye lokacin da ya aikata laifin.

An miƙa lamarin zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka domin ci gaba da bincike, kuma za a gurfanar da shi a kotu nan ba da jimawa ba.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *